Hukumar Zaɓe ta Zambiya ta dakatar da ƙirga ƙuri’u a faɗin ƙasar bayan samun rahotannin tashin hankali a wasu yankuna bayan zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar ranar Alhamis.
Babban Jami’in Zaɓe, Brown Kasaro, ya ce an ɗauki matakin ne bayan an kai wa wasu jami’an zaɓe hari, tare da rahotannin satar takardun zaɓe da akwatunan ƙuri’a a wasu wurare.
Ya ce za a sake duba matakin dakatar da ƙirga ƙuri’un cikin sa’o’i 24, yayin da hukumomi ke nazarin yanayin tsaro tare da yanke shawarar matakin da ya dace na ci gaba da ƙirga ƙuri’un.
Matakin ya haifar da damuwa kan gaskiya da sahihancin tsarin zaɓe, yayin da ake jiran hukumar zaɓen ta sanar da sakamakon hukumance na zaɓen shugaban ƙasa da ake sa ido sosai a kai.
A nasa ɓangaren, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar adawa, Brian Mundubile, ya bayyana matakin dakatar da ƙirga ƙuri’un a matsayin abin da ya matuƙar damu da shi.
Mundubile ya yi kira da a tabbatar da cikakken gaskiya da bayyana komai a tsarin zaɓen, bayan Hukumar Zaɓe ta Zambiya ta sanar da dakatar da ƙirga ƙuri’u a faɗin ƙasar sakamakon rahotannin tashin hankali.
Mundubile ya kuma yi iƙirarin cewa alamomin farko na sakamakon zaɓen na nuna cewa shi ne ya yi nasara a zaɓen shugaban ƙasa, tare da samun rinjaye na kujerun Majalisar Dokoki.
Ya buƙaci hukumomi su tabbatar da cewa jinkirin sanar da sakamakon bai lalata amincewar jama’a da tsarin zaɓe ba, tare da yin kira da a gudanar da sahihin tantance ƙuri’u sannan a sanar da ingantaccen sakamakon zaɓen cikin lokaci.