An ceto wasu ma’aikata biyu da ransu daga tashar samar da wutar lantarki ta ruwa ta Trishuli 3A a Nepal, sama da mako guda bayan wata mummunar ambaliyar ruwa ta kwatsam ta afku a yankin tsaunukan Himalaya.
An bayyana ma’aikatan da aka ceto da sunayen Sanjaya Shah da Kabir Maharjan, inda hukumomi suka ce an kwashe su ta jirgin sama zuwa wani asibiti a birnin Kathmandu domin samun kulawar lafiya.
Dukkansu sun samu raunuka a hannaye da ƙafafuwa, wadanda hukumomi suka ce mai yiwuwa sun samu ne sakamakon yadda suka shafe kwanaki suna rarrafe a cikin wani rami da ke karkashin kasa.
Masu aikin ceto sun ce sun ji muryoyin wasu mutane da sanyin safiyar Juma’a, lamarin da ya kara fata cewa za a iya ceto aƙalla wasu mutane 39 da ake kyautata zaton suna cikin wannan ramin.
Hotunan bidiyo sun nuna lokacin da masu aikin ceto suka fitar da ma’aikatan biyun daga cikin ramin zuwa waje cikin aminci.
Sai dai har yanzu ana fargabar cewa fiye da mutane 150 na iya kasancewa a makale a wasu wurare da ke da nasaba da tashoshin samar da wutar lantarki ta ruwa a Nepal.
Ɗan’uwan ɗaya daga cikin ma’aikatan da aka ceto ya bayyana farin cikinsa da jin daɗinsa bayan samun labarin cewa an gano ɗan uwansa da rai.
Masu aikin ceto na ci gaba da gudanar da bincike da aikin kwashe mutanen da ake zargin ambaliyar ta rutsa da su a yankin.