Ƙungiyar tsaro ta NATO ta ce a shirye take ta tunkari duk wata barazana da Iran za ta iya yi, tana mai cewa za ta ɗauki matakan da suka dace domin kare ƙasashe mambobinta.
Wani jami'in NATO ne ya bayyana hakan yayin da yake mayar da martani kan wani rahoto da jaridar Financial Times ta wallafa, wanda ya ce Iran na iya kai hari kan sansanonin sojojin Amurka da ke Turai idan Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ƙara tsananta matakan soji kan Tehran.
Jami'in NATO ya ce tsarin ƙungiyar na dakile barazana da kare kai yana da ƙarfi kuma yana aiki yadda ya kamata.
Ya ƙara da cewa hakan ya bayyana a farkon wannan shekarar, lokacin da tsarin tsaron sararin samaniyar NATO ya yi nasarar tare makamai masu linzami da Iran ta harba zuwa Turkiyya a lokuta huɗu daban-daban.
A cewar Financial Times, wasu majiyoyi da ke da kusanci da gwamnatin Iran sun ce Tehran na nazarin yiwuwar kai hari kan wuraren sojan Amurka da ke Turai idan Trump ya ƙara tsananta yaƙin.
Jaridar ta ce Iran na duba hanyoyin da za ta iya amfani da su wajen ƙara tsananta rikicin, yayin da sojojinta ke tantance kadarorin Amurka da ke wasu ƙasashen Turai.
Rahoton ya ce wasu majiyoyi biyu da ke da masaniya kan gwamnatin Iran sun bayyana cewa sojojin ƙasar sun tantance wasu kadarorin Amurka da ke ƙasashen kudu maso gabashin Turai, ciki har da Bulgaria.
Bulgaria ta ba da izinin amfani da ɗaya daga cikin sansanonin sojinta a watan da ya gabata domin ɗaukar mai ga jiragen saman Amurka.
Sai dai NATO ta jaddada cewa tana ci gaba da sa ido kan duk wata barazana da za ta iya shafar ƙasashe mambobinta, tare da tabbatar da cewa tana da shirye-shiryen da suka dace domin kare su.