Iyayen yaran da aka sace a jihar Borno sun gudanar da zanga-zanga a garin Uba ranar Alhamis, domin neman gwamnatin Najeriya ta gaggauta ceto kusan yara 100 da ake tsare da su a hannun masu garkuwa da mutane a yankin.
A ranar 15 ga watan Mayu, wasu mahara da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne suka kai hari wata makaranta da ke ƙauyen Mussa, kusa da dajin Sambisa, inda suka sace kimanin ɗalibai 45, ciki har da ƙananan yara. Har yanzu dai yaran na hannun masu garkuwa da su.
Zanga-zangar ta nuna irin damuwar da iyaye ke ciki game da ci gaba da sace mutane da hare-haren ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP, duk da kasancewar jami’an tsaro a yankin.
Ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP sun shafe sama da shekaru 15 suna kai hare-hare da kuma sace ɗalibai a makarantun yankin.
Baya ga sace ɗaliban ƙauyen Mussa, an kuma kai hari wata makaranta da ke ƙauyen Lassa a ranar 29 ga watan Yuni, inda aka sace ɗalibai 36 da wani malami. Har yanzu su ma suna hannun masu garkuwa da su.
A watan da ya gabata ne hukumomin Najeriya suka samu nasarar kuɓutar da wasu ɗalibai da malamai da aka yi garkuwa da su a jihar Oyo, da ke kudu maso yammacin ƙasar.