Gwamnatin Jihar Nasarawa ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da masu zuba jari domin tabbatar da nasarar noman shinkafa a babbar gonar Jangwa-Agwatashi da ke ƙaramar hukumar Obi.

Matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na bunƙasa noman shinkafa, ƙara samar da abinci da kuma tabbatar da wadatar abinci a jihar.

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ziyarci gonar tare da wakilan kamfanonin da ke da hannu a aikin, inda ya sanar da faɗaɗa haɗin gwiwar domin kauce wa tsaiko da tabbatar da dorewar noma a gonar.

A ƙarƙashin sabon tsarin, wani daga cikin kamfanonin zai kula da sarrafa da niƙa shinkafar, yayin da ɗayan mai zuba jari zai ɗauki nauyin muhimman matakan noma, tun daga dasa shinkafa, shirya ƙasa da harrow, har zuwa girbi.

Gwamnatin jihar ta ce ta riga ta cika nata ɓangaren na yarjejeniyar, ciki har da share gonar da samar da sauran kayan aikin da ake buƙata domin fara noma.

Gwamna Sule ya bayyana kwarin gwiwar cewa haɗin gwiwar zai haifar da sakamakon da ake fata, tare da ƙarfafa ƙoƙarin jihar na tabbatar da wadatar abinci.

A wannan zangon noman, an zaɓi nau'ikan shinkafa na FARO 54 da FARO 9, waɗanda ake sa ran za su nuna girma kuma su kasance a shirye domin girbi cikin ƙasa da kwanaki 100.

A wani ɓangare na ziyarar, Gwamna Sule ya duba ayyukan gina hanyoyin karkara da sabuwar gadar da aka kammala ginawa wadda ta haɗa al'ummomin manoma da ke Awe, domin sauƙaƙa zirga-zirga da jigilar amfanin gona zuwa kasuwanni.

Har ila yau, an bayyana yankin a matsayin ɗaya daga cikin wuraren da suka dace da kafa wani bataliyar soji a Jihar Nasarawa.