Kamfanin motocin haya ta manhaja, Uber, ya sanar da dakatar da ayyukansa a Najeriya da Uganda daga Laraba, 2 ga Satumban 2026, bayan shafe sama da shekaru goma yana gudanar da harkokinsa a Najeriya.
Uber ta ce ta ɗauki wannan mataki ne bayan gudanar da cikakken nazari kan abubuwan da ta sa a gaba a harkokin kasuwanci da kuma dabarun zuba jari na kamfanin.
A wata sanarwa da kamfanin ya aikewa BBC, Uber ta ce dakatarwar ta shafi Najeriya da Uganda kaɗai, kuma ba za ta yi tasiri kan ayyukanta a sauran ƙasashen Afirka ba.
Kamfanin ya ce abin da ya fi ba shi muhimmanci a yayin wannan sauyi shi ne tallafa wa direbobi, masu amfani da manhajar da ma’aikatansa na cikin gida.
Uber ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da saka hannun jari a yankin Afirka ta Kudu da Hamadar Sahara, inda take ganin akwai damar bunƙasar kasuwanci a dogon lokaci.
Rahotanni sun ce wasu masu amfani da manhajar a Najeriya sun riga sun karɓi saƙonnin imel daga kamfanin da ke sanar da su game da dakatar da ayyukan.
Sai dai cibiyar taimakon abokan hulɗar Uber za ta ci gaba da aiki har zuwa 24 ga Satumba, domin amsa tambayoyi da kuma taimaka wa waɗanda abin ya shafa wajen warware matsalolin da suka shafi rufe ayyukan.
Uber ta shafe fiye da shekaru goma tana aiki a Najeriya. Yanzu ta fice daga kasuwar ƙasar.