Kamfanin dillancin labaran Reuters ya rawaito cewa wani jami’in Amurka ya tabbatar da cewa Iran ta harba makamai masu linzami da kuma jiragen sama marasa matuƙa zuwa wasu ƙasashe makwabta, ciki har da Bahrain da Kuwait.

 

Tuni rundunar IRGC ta Iran ta sanar cewa ta kai hari kan wuraren sojojin Amurka, inda ta ce ta nufi sansanin Ali al-Salem da ke Kuwait, da kuma hedikwatar rundunar ruwa ta Amurka da ke Bahrain.

 

Rundunar ta ce ta kai waɗannan hare-hare ne da makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa.