Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya san wane ne jagora a tsakaninsu, yana mai jaddada cewa dangantakar da ke tsakanin shugabannin biyu tana nan daram duk da rahotannin da ke cewa akwai saɓani a kan wasu batutuwa.
Trump ya bayyana hakan ne a wata gajeriyar hira da ya yi da kafar Axios, inda ya ce suna da kyakkyawar alaƙa, kuma Netanyahu ya fahimci matsayin jagoranci da ke tsakaninsu.
Kalaman shugaban Amurkan na zuwa ne a daidai lokacin da ake sa ran Netanyahu zai kai ziyara Fadar White House a cikin kwanaki masu zuwa.
Idan ziyarar ta tabbata, za ta kasance ganawa ta farko tsakanin shugabannin biyu tun bayan fara rikicin da ya shafi Iran.
Rahotanni sun nuna cewa duk da kyakkyawar alaƙar da ke tsakaninsu, akwai bambancin ra'ayi kan wasu batutuwan tsaro, musamman game da rikicin Iran da kuma matakan da Isra'ila ke ɗauka a Lebanon.