Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna ta yi Allah wadai da kisan wasu matafiya biyu, Muhammadu Sani da abokinsa Aliyu Mohammed, dukkansu mazauna ƙauyen Umar da ke ƙaramar hukumar Igabi, waɗanda wasu fusatattun mutane suka kashe bisa zargin sata.

A wata sanarwa da Jami'in Hulɗa da Jama'a na Rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce marigayin da abokinsa na kan hanyarsu ta zuwa Tudun Wada da ke Zariya ne domin duba wani baffansu da ke kwance jinya, inda suke tafiya da sabuwar babur.

Sanarwar ta ce wasu mutane sun yi musu kuskuren zargin cewa ɓarayi ne, kuma duk da ƙoƙarin da suka yi na bayyana kansu da roƙon a saurare su, taron jama'a ya lakada musu duka har suka mutu.

Da samun rahoton faruwar lamarin, jami'an 'yan sanda daga ofishin Birnin Yero suka gaggauta kai ɗauki, inda suka kama mutane shida da ake zargi da hannu a wannan aika-aika.

Rundunar ta ce waɗanda aka kama sun amsa hannu a aikata laifin, kuma suna ci gaba da tsare a hannun 'yan sanda, yayin da ake faɗaɗa bincike domin kamo sauran mutanen da suka shiga cikin kisan.

Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya yi Allah wadai da lamarin, tare da alƙawarin cewa duk wanda aka samu da hannu a wannan kisa, ba tare da la'akari da matsayinsa ba, za a gurfanar da shi a gaban kotu domin fuskantar hukunci.

Ya kuma gargaɗi al'umma da su guji ɗaukar doka a hannunsu, yana mai jaddada cewa babu wanda ke da ikon hukunta wanda ake zargi da laifi ba tare da bin matakan doka ba.

Kwamishinan ya tunatar da jama'a cewa a bisa doka, duk wanda ake zargi da aikata laifi ana ɗaukarsa a matsayin marar laifi har sai kotu ta tabbatar da akasin haka.

Ya yi kira ga mazauna jihar da su riƙa kai rahoton duk wanda suke zargi da aikata laifi ga mafi kusa da ofishin 'yan sanda ko sauran hukumomin tsaro domin gudanar da bincike da ɗaukar matakin da doka ta tanada.