Wata kotu da ke Port Sudan ta yanke wa jagoran rundunar Rapid Support Forces (RSF), Mohamed Hamdan Dagalo, wanda aka fi sani da Hemedti, hukuncin ɗaurin rai da rai.
Kotun ta yanke hukuncin ne a shari'ar da aka gudanar ba tare da Hemedti ya halarta ba, inda ta same shi da laifukan kisan ƙare dangi, aikata laifukan yaƙi, laifukan cin zarafin bil'adama, da kuma kai hare-hare kan fararen hula.
Hukuncin, wanda aka yanke ranar Lahadi, 12 ga Yulin 2026, shi ne mafi tsauri da aka taɓa yanke wa jagoran RSF tun bayan ɓarkewar yaƙin Sudan a shekarar 2023.
Shari'ar ta fi mayar da hankali kan kisan tsohon gwamnan Yammacin Darfur, Khamis Abbakar, wanda aka kashe a shekarar 2023 bayan an yi zargin cewa an yi garkuwa da shi. Kafin rasuwarsa, Abbakar ya zargi dakarun RSF da hannu wajen aikata kisan ƙare dangi a yankin.
Kotun ta kuma yanke hukunci kan wasu manyan jami'an RSF da suka haɗa da Abdelrahim Dagalo da Algoney Dagalo, waɗanda dukkansu aka yi wa shari'ar ba tare da sun halarta ba.