Hukumar Kula da Madatsun Ruwa ta Najeriya (NIHSA) ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar samun ambaliya a wasu sassan jihohi 14 na ƙasar tsakanin 14 zuwa 20 ga watan Yuli, sakamakon hasashen cikar koguna da tashin ruwa.
Darakta Janar na hukumar, Umar Mohammed, ya bayyana cewa rahotannin hasashen da hukumar ta tattara sun nuna yiwuwar ruwa ya mamaye wasu yankuna, musamman waɗanda ke kusa da manyan koguna da madatsun ruwa.
A cewarsa, daga cikin wuraren da ake sa ran za su fi fuskantar barazanar ambaliya akwai Saminaka da ke kusa da Kogin Karam, yankin Madatsar Waya da ke bakin Kogin Waya, da kuma yankin Amber da ke kusa da Kogin Amber.
Jihohin da NIHSA ta ce na iya fuskantar matsakaicin haɗarin ambaliya sun haɗa da:
- Adamawa
- Akwa Ibom
- Anambra
- Bauchi
- Benue
- Borno
- Cross River
- Edo
- Enugu
- Imo
- Kaduna
- Legas
- Neja
- Filato
Hukumar ta yi gargadin cewa idan ba a ɗauki matakan kariya cikin gaggawa ba, ambaliyar na iya haddasa asarar rayuka da dukiyoyi tare da lalata makarantu, cibiyoyin lafiya, kasuwanni da sauran muhimman ababen more rayuwa.
Saboda haka, NIHSA ta shawarci mazauna yankunan da ke cikin haɗari da su koma wurare masu aminci idan buƙatar hakan ta taso, su riƙa share magudanan ruwa, su guji ketare hanyoyin da ruwa ya mamaye, sannan su ci gaba da bibiyar sanarwar hasashen ambaliya da hukumar ke fitarwa.
Hakazalika, hukumar ta buƙaci gwamnatocin jihohi da hukumomin ba da agajin gaggawa su kasance cikin shirin ko-ta-kwana, tare da tanadin matakan kwashe jama'a daga yankunan da ke cikin haɗari da kuma ƙara wayar da kan al'umma kan hanyoyin kare kai daga ambaliya.