Iran ta gargaɗi ƙasashen yankin Gulf kada su bari Amurka ta yi amfani da yankunansu ko sararin samaniyarsu ko kuma gaɓoɓin ruwansu wajen kai hari cikin ƙasar.
Tehran ta ce irin wannan mataki zai janyo mummunan sakamako ga waɗannan ƙasashe.
Shugaban kwamitin harkokin cikin gida na Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Saleh Jokar, ya ce idan Amurka ta yi amfani da yankunan waɗannan ƙasashe wajen kai hari kan Iran, to za su fuskanci mummunar asara.
A wani ɓangaren kuma, Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta ce sake kakaba takunkumi kan harkokin sufurin ruwa zai zama saɓa wa yarjejeniyar da aka ƙulla tsakanin Tehran da Washington.
Sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta kuma zargi Amurka da aikata laifukan yaƙi, tana mai nuni da hare-haren da aka kai wa muhimman cibiyoyin fararen hula da kuma wuraren samar da ayyukan jama’a a matsayin misalai.
Iran ta ce wuraren da aka kai wa hari sun haɗa da cibiyar lafiya ta rundunar soji ta Brigade na 388 da cibiyar ajiye kayayyaki da Hoveizeh da kuma wasu wurare daban.