Ma'aikatar Lafiya ta Iran ta ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon hare-haren sama da Amurka ta kai ya haura mutum 50, yayin da sama da mutum 500 suka jikkata.
Shugaban Cibiyar Hulɗa da Jama'a ta Ma'aikatar, Hossein Kermanpour, ya bayyana a shafinsa na X cewa zuwa ƙarfe 7:00 na safiyar ranar 18 ga watan Yuli, hare-haren sun yi sanadin jikkatar mutum 517 tare da mutuwar fiye da mutum 50.
A cewarsa, daga cikin waɗanda suka jikkata akwai mata 35 da yara 19 da shekarunsu ba su kai 18 ba.
Ya kuma ce cikin waɗanda suka mutu akwai mata biyar da yara biyu da ba su kai shekara 18 ba.
Kermanpour ya ƙara da cewa an sallami mutum 468 daga asibitoci bayan sun samu kulawar lafiya, yayin da mutum 33 ke ci gaba da karɓar magani.
Sai dai har zuwa lokacin wallafa wannan labari, Amurka ba ta fitar da wata sanarwa da ta tabbatar ko ta yi martani kan alkaluman da Iran ta bayyana ba.