Jam'iyyar ADC ta zaɓi ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar tarayya ta Ille/Gwadabawa, Bello Ambarura, a matsayin ɗan takarar mataimakin gwamnan jihar Sakkwato a zaɓen gwamna na shekarar 2027.


Jam'iyyar ta sanar da naɗin ne cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin, wadda Sakataren Yaɗa Labarai na ADC na jihar Sakkwato, **Lamir Aminu**, ya sanya wa hannu. Ya ce Ambarura zai yi takara tare da ɗan takarar gwamna na jam'iyyar, **Manir Muhammad Dan-Iya**.


Aminu ya bayyana cewa an yi wannan naɗi ne bayan gudanar da tattaunawa mai zurfi a cikin jam'iyyar, kuma ya yi daidai da tanadin Sashe na 187(1) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na shekarar 1999.


A cewarsa, wannan mataki yana nuna aniyar jam'iyyar ta gabatar da shugabanci mai ƙwarewa, nagarta da kuma mai fifita muradun al'ummar jihar Sakkwato.


Ya ce, *"An yi wannan naɗi ne bisa tanadin Sashe na 187(1) na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), bayan tattaunawa mai faɗi da kuma yin nazari kan irin halayen da ake buƙata domin gina ƙungiyar shugabanci mai ƙarfi, ƙwarewa da kuma mai yi wa al'umma hidima a jihar Sakkwato."*