Gwamnatin Qatar ta miƙa wa Majalisar Ɗinkin Duniya da Kwamitin Tsaro wasiƙu inda ta dora cikakken alhakin hare-haren da aka kai kan ƙasarta a kan Iran, tare da neman a biya ta diyya kan dukkan ɓarnar da aka yi.
A cikin wasiƙun, Qatar ta ce Iran ta kai hari kan wani jirgin dakon mai a kusa da mashigar Hormuz a ranar 7 ga Yulin 2026, sannan ta sake harba makamai masu linzami zuwa cikin ƙasar a ranakun 12 da 17 ga Yuli.
Jami'an Qatar sun ce mutane uku, ciki har da wani yaro, sun jikkata a harin ranar 12 ga Yuli bayan gutsuttsuran makaman da aka tarwatsa suka faɗo a wuraren zama.
Qatar ta bayyana hare-haren a matsayin ƙeta huruminta da 'yancin kai na ƙasa, tana mai cewa sun zama barazana kai tsaye ga tsaro da cikakken ikon ƙasar.
Haka kuma, gwamnatin Qatar ta jaddada cewa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar duk matakan da suka dace domin kare ikon ƙasarta, tsaron al'ummarta da rayukan 'yan ƙasa.
A nata ɓangaren, Iran ta ce hare-haren da take kai wa a yankin na nufin cibiyoyin sojojin Amurka da dakarunta da ke jibge a wasu ƙasashen yankin, ba fararen hula ba.