Mai magana da yawun Gwamnatin Birnin Tehran, Abdul Motahar Mohammadkhani, ya bayyana cewa ana sa ran kammala dukkan ayyukan da suka shafi sake gina da gyaran gidajen da yaƙin baya-bayan nan ya lalata kafin ƙarshen watan Yuli.

Ya ce an samu ci gaba da ya kai kusan kashi 40 cikin 100 a aikin sake gina gidajen da lalacewarsu ta yi muni har ta kai ga buƙatar rushe su gaba ɗaya tare da sake ginawa.

A cewarsa, gidaje kusan 51,000 ne suka samu matsaloli daban-daban sakamakon yaƙin, lamarin da ya sa gwamnatin birnin ta ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalar.

Mohammadkhani ya ƙara da cewa aikin gyaran gidajen da suka samu ƙananan lalacewa ya kai kashi 97 cikin 100, kuma ana sa ran kammala sauran ayyukan da suka rage kafin ƙarshen wannan mako.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Birnin Tehran ce ke jagorantar babban aikin sake gina gidajen da suka lalace, tare da daidaita ayyukan tallafawa waɗanda rikicin ya shafa.

Game da iyalan da ke zaune a matsugunan wucin gadi, ya ce har yanzu ba a kayyade ranar da za su bar otal-otal da aka tanadar musu ba.

Sai dai ya bayyana cewa adadin iyalan da ke matsugunan ya ragu sosai, inda daga sama da iyalai 2,300 da suka nemi mafaka a lokacin da yaƙin ya fi tsanani, yanzu adadin ya sauka zuwa iyalai 1,629.