Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta sanar da ware dala miliyan 3.5 (kimanin Naira biliyan 5) domin tallafawa shirye-shiryen tattara bayanai da rahotanni kan take hakkin ‘yancin addini da tashe-tashen hankula masu alaka da addini a Najeriya.

Shirin, wanda Ofishin Kula da ‘Yancin Addini na Kasa da Kasa (IRF) ya sanar a ranar 22 ga Mayu, 2026, na da nufin karfafa ayyukan kungiyoyi da cibiyoyi da ke sa ido tare da rubuta bayanai kan hare-haren da suka shafi addini da akida a fadin Najeriya.

A cewar sanarwar, za a gudanar da aikin na tsawon watanni 24 zuwa 48, kuma za a bai wa wata kungiya ko hukuma guda damar aiwatar da shi ta hanyar tallafi ko hadin gwiwa.

Za a rika tattara bayanai kan take hakkin addini

Gwamnatin Amurka ta bayyana cewa shirin zai taimaka wajen sa ido da tattara hujjoji kan cin zarafi da take hakkin addini da kungiyoyin gwamnati ko wadanda ba na gwamnati ba ke aikatawa.

Sanarwar ta ce:

"Muna neman kungiyoyin da za su taimaka wajen inganta tattara bayanai da rahotanni kan take hakkin ‘yancin addini a Najeriya domin tabbatar da adalci, wayar da kai da kuma adana tarihin abubuwan da suka faru."

An ambaci Boko Haram da wasu kungiyoyin masu dauke da makamai

Takardar ta yi nuni da cewa hare-haren da kungiyar Boko Haram, ISIS ta Yammacin Afirka da wasu kungiyoyin masu dauke da makamai ke kaiwa sun shafi Musulmi da Kiristoci.

Ta ce masu rajistar bayanai, kungiyoyin kare hakkin bil’adama, shugabannin addinai, masana, ‘yan jarida da wadanda suka tsira daga hare-hare sun bayar da gudunmawa wajen samar da hujjojin da ke nuna girman matsalar.

Zargin gazawar hukumomin Najeriya

Sanarwar ta kuma yi zargin cewa hukumomin Najeriya ba sa mayar da martani cikin gaggawa ko yadda ya kamata ga hare-haren da ake kai wa al’umma da wuraren ibada.

A cewar rahotannin kungiyoyin farar hula da Amurka ta ambata, wannan yanayi na kara haifar da rashin hukunta masu laifi, wanda ke karfafa ci gaba da aikata hare-hare da kuma haddasa karin korar jama'a daga muhallansu.

Haka kuma, sanarwar ta ce akwai rahotanni masu inganci da ke nuna cewa wasu jami’an tsaro sun kai samame wuraren ibada yayin neman wadanda ake zargi da aikata laifuka, lamarin da ya jikkata wasu malamai da masu ibada.

Trump ya ayyana Najeriya a matsayin kasar da ke da matsalar ‘yancin addini

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta bayyana cewa wannan shiri ya biyo bayan matakin Shugaban Amurka, Donald Trump, na ayyana Najeriya a watan Nuwamban 2025 a matsayin “Country of Particular Concern” (CPC) saboda zargin take hakkin ‘yancin addini.

Amurka ta ce wannan mataki ya kara haskaka matsalolin da ake zargin sun dade suna faruwa tare da kara muni.

Gwamnatin Najeriya ta musanta zargin

Sai dai gwamnatin Najeriya ta yi watsi da zarge-zargen cin zarafin addini, tana mai cewa matsalar rashin tsaro tana shafar dukkan ‘yan kasa ba tare da la’akari da addininsu ba.

Gwamnatin ta kuma jaddada cewa tana ci gaba da hada kai da Amurka wajen yaki da ta’addanci da kuma aiwatar da gyare-gyaren tsaro domin inganta zaman lafiya a kasar.

Kungiyoyin da ke son neman wannan tallafi za su iya gabatar da bukatunsu kafin ranar 9 ga Yuli, 2026, yayin da Amurka ta bukaci a mayar da hankali musamman ga jihohin yankin Middle Belt da wasu jihohi hudu da za a zaba domin gudanar da aikin.