Al’ummar Jihar Ekiti da ke yankin Kudu maso Yammacin Najeriya sun fara kaɗa ƙuri’unsu a zaɓen gwamna da ake gudanarwa domin zaɓar wanda zai jagoranci jihar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa.
Tun da safiyar ranar zaɓen ne masu jefa ƙuri’a suka fara tururuwa zuwa rumfunan zaɓe domin amfani da haƙƙinsu na zaɓen shugabanni.
Rahotanni sun nuna cewa ‘yan takara 14 ne ke fafatawa a zaɓen, ciki har da gwamna mai ci, Biodun Oyebanji, wanda ke neman wa’adi na biyu a kan karagar mulki.
Haka kuma, zaɓen ya ja hankali saboda kasancewar huɗu daga cikin ‘yan takarar sun zaɓi mata a matsayin mataimakansu, lamarin da ke nuna ƙarin shiga mata cikin harkokin siyasa da shugabanci.
An fara kaɗa ƙuri’a da misalin ƙarfe 8:30 na safe, yayin da ake sa ran rufe rumfunan zaɓe da ƙarfe 2:30 na rana.
Fiye da masu zaɓe miliyan ɗaya ne ake sa ran za su kaɗa ƙuri’unsu a rumfunan zaɓe 2,445 da aka tanada a faɗin jihar.
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka dace domin tabbatar da gudanar da zaɓen cikin gaskiya, adalci da kuma lumana.
A gefe guda kuma, jami’an tsaro sun bazu a sassa daban-daban na jihar domin tabbatar da tsaro da kuma hana duk wani abu da ka iya kawo cikas ga tsarin zaɓen.
Ana sa ran za a fara tattara sakamakon zaɓen bayan kammala kaɗa ƙuri’a da rufe rumfunan zaɓe.