Rundunar 'Yan Sandan Najeriya ta tabbatar da cewa dalibai 36 da wani ma'aikacin makaranta guda ɗaya har yanzu suna hannun masu garkuwa, bayan harin da aka kai wata makaranta a yankin Lassa, ƙaramar hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno.

A cewar hukumomin tsaro, an ceto mutum 10, ciki har da mataimakin shugaban makarantar, yayin da ake ci gaba da aikin neman da kubutar da sauran.

Lamarin ya faru ne a lokacin da ɗaliban ke rubuta jarabawar NECO, kuma jami'an tsaro sun ce ana ci gaba da bincike da kuma ayyukan ceto a yankunan da abin ya shafa.